Thursday, February 5
Shadow

Idan ADC ta tsayar dani takara babu shakka zan kayar da Shugaba Tinubu zabe a 2027>>Rotimi Amaechi

Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya bayyana cewa, idan jam’iyyar ADC ta bashi takarar shugaban kasa a zaben 2027 tabbas zai kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Ya bayyana hakane a kafarsa ta X.

Zan canja kundin tsarin mulki, zan kawo ƙarshen cin hanci cikin wata idan na zama shugaban ƙasa – Amaechi

Tsohon Ministan Sufurin Najeriya Rotimi Amaechi ya jaddada cewa zai canja kundin tsarin mulkin Najeriya idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a shekarar 2027.

Amaechi ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a shafin sa na X a ranar Juma’a, inda yace zai kawo karshen matsalar cin hanci a cikin wata daya ko ya sauka daga mulki.

Karanta Wannan  Shiekh Professor Isa Ali Pantami ya biyawa 'yar marigayi Sheikh Albani bashin da ake binta bayan ya jagoranci yin sulhu

Amaechi ya kuma bayyana Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin lalataccen shugaban hukumar zaɓe a tarihin Najeriya.

Daga Usman Salisu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *