Saturday, May 10
Shadow

Ji ainahin abinda ya faru tsakanin Minista Tugga da Mataimakin gwamnan jihar Bauchi(wanda aka ce ya zabgawa Ministan Mari) wanda sai da Mataimakin shugaban kasa ya shiga tsakani

Rahoton Marin da mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Auwal Jatau yawa Ministan Harkokin kasashen Waje, Yusuf Tuggar na daya daga cikin wadanda suka dauki hankula a yau.

Saidai daga baya Mataimakin gwamnan ta bakin me magana da yawunsa, Muslim Lawal ya musanta hakan.

Amma a wata majiya da muka samo da kafar Sahara Reporters tace tabbas an yi musayar yawu tsakanin Mataimakin gwamnan da Ministan a cikin motar bas data daukesu zuwa fadar Me martaba Sarkin Bauchi.

Rahoton yace ana tsaka da tafiyane sai aka ga fastar Ministan sai gwamna yace zasu yi maganinsa saboda rashin kunyar da yakewa shuwagabannin jam’iyyar jihar.

Saidai Tuggar ya mayar da martanin cewa jihar Bauchi ba kayan kowa bace, hakan yasa mataimakin gwamnan yayi kokarin kaiwa gareshi amma sai jami’an tsaron mataimakin shugaban kasa suka hanashi saboda mataimakin shugaban kasar na zaune tsakaninsu.

Karanta Wannan  Kalli Hoto: Tsohuwar 'yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Rahoton yace ko da aka tashi komawa, mataimakin gwamnan bai koma a motar bas din data kaisu fadar sarkin ba dan kaucewa kara yin rikici da Ministan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *