
Hukumar Hisbah a Kano ta lalata wajan da aka rika yada rade-radin cewa wai an ga sahun Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) a Kano.
Wajan dai yana Dakata ne inda aka ga bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sadarwa mutane suna rububin sha da wanka da ruwan wajan.
Mataimakin kwamandan Hisbah na jihar Kano, Muhahideen Aminudeen ya bayyana cewa ko da suka ji labari, sun je wajan inda suka ilimantar da mutanen wajen cewa wannan ikirari karyane.
Sun gayawa mutanen cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) bai taba zuwa Afrika ba.
Ya jawo hankalin iyaye da su rika baiwa ‘ya’yansu ilimi na Addini dan su rika banbance gaskiya da karya.
Ya kuma bayyana cewa shan irin wannan ruwa ma na da hadari ga lafiyar mutum.