Thursday, December 18
Shadow

Kalli Bidiyon: Kalar Gaisawar da shugaba Traore yayi da Wakilan Najeriya da suka je bashi hakuri ta dauki hankula

A jiyane wakilan Gwamnatin Najeriyar suka je kasar Burkina Faso dan baiwa shugaba Ibrahim Traore Hakuri kan jirgin Najeriya da ya shiga kasar da sojoji 11 ba tare da izini ba.

Kalar Gaisuwar da suka yi da shugaba Traore ta dauki hankula sosai.

Saidai wasu ‘yan Najeriya sun rika mamakin wai hakuri kawai kasar ta Burkina Faso ke son Najeriya ta bata kamin a saki sojojin.

A jiyan dai an saki sojojin na Najeriya bayan ziyarar wakilan Najeriyar.

Wani abu da ya kara daukar hankalin mutane shine yanda wakilan suka shaidawa Gwamnatin kasar Burkina Faso cewa kalamai marasa dadi da wasu ‘yan Najeriya suka rika fadi akan kasar Burkina Faso ba da yawun Gwamnati bane.

Karanta Wannan  Gwamnan Jihar Katsina, Malam Umar Dikko Radda, Ya ƙaddamar da motocin sufuri a Jihar Katsina
@livenewsafricamedia

Présidencedufaso ibrahimtraore Burkinafaso Lna livenewsafrica

♬ son original – Live News Africa – Live News Africa
https://twitter.com/Aesalerte/status/2001386700745122190?t=uasiW6qqz5kSpejJjGcqDw&s=19

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *