Tuesday, March 18
Shadow

Kalli bidiyon yanda sojoji suka je ofishin NEPA suka kwashe ma’aikatan zuwa barikinsu bayan da aka yanke musu wutar Lantarki

Rahotanni daga legas na cewa, hukumar sojojin sama sun kai farmaki ofishin hukumar wuta ta jihar, Ikeja Electric inda suka ci zarafin ma’aikatan hukumar ciki hadda shugabar ma’aikatar.

Lamarin ya farune bayan da Hukumar sojin sama dake barikin Sam Ethan Base aka dauke musu wuta saboda kasa biyan bashin sa ake binsu.

Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta ya nuna yanda sojojin suka ci zarafin wasu ma’aikatan hukumar.

Karanta Wannan  Al'ummar Jihar Yobe Da Ma Na Nijeriya Baki Daya Matukar Kaduwa Tare Da Nuna Jimaminsu Kan Mutane Sama Da Dari Da 'Ýan Boķo Hàŕàm Šùķa Ķàšhè A Kauýen Mafa Dake Karamar Hukumar Tarmuwa A Jihar Yobe

Shugabar ma’aikatar, Folake Soeten tace sun kamata sun kulleta a cikin but din mota a yayin cin zarafin.

Saidai hukumar sojin saman na kokarin cewa bata san wane sojoji ne suka je suka aikata wannan lamari ba.

Saidai dan jarida, Oseni Rufai ya bayyana cewa, karyane hukumar sojojin saman tace bata san wadanne sojoji ne suka je suka aikata wannan lamari ba.

Yace akwai takarda da wani kwamandan sojojin yayi barazanar daukar mataki akan hukumar wutar.

Karanta Wannan  Makaranta a Najeriya ta kori ɗalibar da ta fallawa malami mari kan ya hanata TikTok

A wata hira da aka yi da daya daga cikin ma’aikatan hukumar wutar ta IKEJA Electric yace da sojojin suka je sun kwace musu wayoyi sannan kuma sun lalata musu kyamarori.

A wata majiyar ma an ce sojojin har wasu kaya suka kwasa suka tafi dasu sannan sun lalata wasu kayan aikin kamfanin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *