Saturday, January 3
Shadow

Kalli bidiyon yanda wani yayi kashin kullin Kwàyòyì 120 da ya hadiya yana shirin fita dasu kasashen waje

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, NDLEA ta kama wani mutum da me suna Mbala Dajou Abuba a filin sauka da tashin jiragen sama na Mallam Aminu Kano dake Kano yana shirin fita da kwayoyi zuwa kasashen waje.

An kama mutumin da ya hadiyi kullun Hodar Iblis da yawa yana shirin fita da ita zuwa Istanbul babban birnin kasar Turkiyya.

Mutumin dan asalin Zaire ne ta kasar Angola kuma an kamashine ranar Talata, February 25, 2025 inda yake shirin hawa jirgin sama zuwa kasar Egypt wanda daga can zai wuce zuwa kasar Turkiyya.

Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya bayyana cewa mutumin yace yana aikin kai sakonnine a kasarsa ta Angola kamin ya fada harkar safarar kwaya.

Karanta Wannan  A hukumance Sanata Kawu Sumaila mai wakiltar mazaɓar Kano ta Kudu ya koma jam'iyyar APC daga NNPP bayan Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Godswill Akpabio ya karanta wasiƙar sauya sheƙarsa a yayin zaman majalisar na yau Laraba

alli Bidiyon anan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *