Friday, December 26
Shadow

Kowa ya Kwantar da Hankalinsa: Trump bai isa ya kawo Khari Najeriya ba sai na amince>>Inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa Amurka bata isa ta kawo Hari Najeriya ba sai da amincewarsa.

Ya bayyana hakane ta bakin me bashi shawara kan sadarwa, Daniel Bwala a hirarsa da manema labarai.

Daniel Bwala yace Keta dokar kasa da kasa ne wata kasa ta kaiwa wata kasa hari ba tare da sanin kasar da aka kaiwa harin ba.

Yace ba’a fahimci abinda Trump ya fada bane, wannan abu ne da zasu warwareshi ta hanyar Diplomasiyya.

Ya bayyana cewa, Suna godiya ga Trump da amincewa da yayi ya sayarwa da Najeriya makamai a zamanin mulkinsa na farko.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Shugaban Nigeriya Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Rome, Italy domin halartar bikin rantsar da sabon Paparoma Pope Leo XIV a ranar Lahadi mai zuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *