Wednesday, March 18
Shadow

Ku Daina Takalarmu, Tinubu zai iya tsige kowane gwamna, na jihar Rivers ne tsautsai ya fada kanshi ya zama na farko>>Tinubu ya gargadi Gwamnoni

Babban lauyan Gwamnati, Lateef Fagbemi ya kare matakin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauka na dakatar da gwamnan jihar Rivers.

Inda yace shugaban kasar na da karfin ikon dakatar da kowanw Gwamna.

Fagbemi ya gargadi gwamnonin cewa duk gwamnan dake neman zama barazana ga Gwamnatin Tinubu na iya fuskantar dakatarwa.

Yace a yau gwamnan jihar Rivers ne a gobe zai iya zama kowane Gwamna.

Ya gargadi cewa babu wanda zasu bari ya mayar da Dimokradiyya abin wasansa.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Tsohon da aka ruwaitoshi yana cewa shine ya gina kabarin Shugaba Buhari, a yanzu ya fito ya ce karya yake bashine ya gina kabarin ba, saidai an zargi cewa tursasashi aka yi ya fadi hakan bayan da yace ba'a biyashi kudin ginin kabarin da yayi ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *