Saturday, December 13
Shadow

Kuma Dai: Jirgin Yakin Sojin Najeriya ya Kàshè ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara

Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, jirgin yakin sojin Najeriya ya kashe ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara.

Shafin Bakatsina ya ruwaito cewa, lamarin ya farune a kauyen Mani dake kamar Hukumar Maru dake jihar.

Yace an kashe manoma 50 da yin garkuwa da mutane 20 a ranar da lamarin ya faru bayan harin ‘yan Bindiga.

Yace jirgin da aka kawo dan ya taimaka a yi maganin ‘yan Bindigar sai ya kare da kashe ‘yan Banga bisa kuskure.

Zuwa yanzu dai Gwamnatin jihar Zamfara da Hukumomin tsaro basu ce uffan ba kan lamarin.

Karanta Wannan  Zan iya mùtùwà a kan APC, in ji tsohon Gwamnan Abia, Uzor Kalu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *