Monday, April 27
Shadow

Kuma Dai: Jirgin Yakin Sojin Najeriya ya Kàshè ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara

Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, jirgin yakin sojin Najeriya ya kashe ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara.

Shafin Bakatsina ya ruwaito cewa, lamarin ya farune a kauyen Mani dake kamar Hukumar Maru dake jihar.

Yace an kashe manoma 50 da yin garkuwa da mutane 20 a ranar da lamarin ya faru bayan harin ‘yan Bindiga.

Yace jirgin da aka kawo dan ya taimaka a yi maganin ‘yan Bindigar sai ya kare da kashe ‘yan Banga bisa kuskure.

Zuwa yanzu dai Gwamnatin jihar Zamfara da Hukumomin tsaro basu ce uffan ba kan lamarin.

Karanta Wannan  Tafiye-Tafiyen da Tinubu yayi sun kawowa Najeriya zuba jari na dala Biliyan $50

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *