Thursday, January 8
Shadow

Ma’aikatan wutar Lantarki zasu tsunduma yajin aiki

Rahotanni na cewa, ma’aikatan wutar lantarki na Abuja zasu tafi yajin aiki.

Ana sa ran lamarin zai saka mutanen jihohin Naija, Kogi, da Nasarawa cikin duhu.

Ma’aikatan kamfamin me suna (AEDC) sun bayyana cewa, zasu tsunduma yajin aikinne saboda kasa cika alkawuran da kamfanin ya dauka bayan da suka yi yajin aiki a watan Nuwamba na shekarar 2024.

A cikin sakon da suka aikawa hukumar kamfanin na AEDC sun Sanar da cewa wannan shine karo na karshe da zasu yi gargadi kuma a koda yaushe zasu iya tsunduma yajin aiki

Karanta Wannan  Insha Allahu Daga Yau Ma Bar Darika Kuma Ina Mai Neman Afuwar Marigayi Sheik Idris Dutsen Tanshi Da Iyalansa Da Dalibansa, Kuma Daga Yau Da Ni Za A Ďìnga Yada Sùññah, Kuma Na Yi Mafarki Na Ga Sheik Idris Dutsen Tanshi A Aljànnah, Inji Umar Ambato

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *