Tuesday, March 18
Shadow

Masu garkuwa da mutane sun sace wata mata a Asibitin dake Kano

Masu garkuwa da mutane sun sace wata mata me shekaru 60 da haihuwa a Asibitin mahaukata dake Dawanau, Karamar hukumar Dawakin Tofa Kano.

Matar me suna Talatu Ali an yi garkuwa da itane a yayin da take jiran ganin Likita.

Dan matar da dan uwanta ne suka kai ta Asibitin, saidai a yayin da suma suke jiran layi ya zo kanta taga likita, sai suka nemeta sama da kasa suka rasa.

Lamarin ya farune ranar February 19, 2025 da misalin karfe 8 na safe, saidai ranar February 21 da misalin karfe 7 na safe an kira danginta inda aka tabbatar musu da cewa an yi garkuwa da itane.

Karanta Wannan  Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam'iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam'iyyar SDP

Hukumar ‘yansandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *