Friday, December 5
Shadow

Matan Jihar Bayelsa sun bayyana takaici da watsi da Shugaba Tinubu yayi dasu bayan da suka masa yakin neman zabe

Mata magoya bayan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun bayyana takaici da jin Haushin watsi da aka yi dasu bayan da sukawa shugaban kasar yakin neman zabe.

Matan sun nemi a sakasu cikin bayar da mukamin da shugaban kasar yake yi.

Matan wadanda suka fito daga jihar Bayelsa sun bayyana hakane ta bakin wakiliyarsu a Abuja ranar Litinin.

Tace a cikinsu akwai kwararrun mata da zasu taimaka wajan cimma muradun gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu idan aka basu dama.

Ta bayyana takaicin yanda aka rasa mata a mukaman siyasa a Gwamnatin Tinubu duk da rawar da suka taka wajan yakin neman zabensa.

Karanta Wannan  Miji ya saki matarshi bayan da mawakin Amurka, Chris Brown ya sumbaceta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *