Wednesday, April 8
Shadow

Mun samar da tsaro sosai a Yankin Arewa, yanzu mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu, sun koma garuruwansu>>Inji Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, jami’an tsaro sun samar da tsaro sosai a yankin Arewa maso gabas da Arewa maso yamma.

Yace Mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu saboda matsalolin tsaro a yanzu sun koma gidajen nasu.

Shugaban yace an samu nasarori sosai a yaki da masu dauke da makamai a sassa daban-daban na kasarnan.

Shugaban ya bayyana hakane yayin da yake jawabin ranar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yanci.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Dan Allah a samu malaman (Gaskiya) su fito su yi bayani, Samarin mu sun dauki fatawar Sheikh Karmawi, idan suka zo neman auren mu sai su ce wai sai sun leka>>Inji Murja Kunya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *