Friday, January 16
Shadow

Mun samar da tsaro sosai a Yankin Arewa, yanzu mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu, sun koma garuruwansu>>Inji Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, jami’an tsaro sun samar da tsaro sosai a yankin Arewa maso gabas da Arewa maso yamma.

Yace Mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu saboda matsalolin tsaro a yanzu sun koma gidajen nasu.

Shugaban yace an samu nasarori sosai a yaki da masu dauke da makamai a sassa daban-daban na kasarnan.

Shugaban ya bayyana hakane yayin da yake jawabin ranar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yanci.

Karanta Wannan  Dodar Ta tabbata, Kowa ya shaida mulkin Adalci na Shugaba Tinubu dan haka 2027 zai zarce>>Ganduje

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *