
Gwamnatin Kano karkashin Abba Kabir Yusuf ta bayyana cewa dubban mutanen da suka taru a wajan komawar Rabiu Musa Kwankwaso Jam’iyyar ADC kudi aka basu.
Kwamishinan yada labarai na Kano, Ibrahim Waiya ne ya bayyana haka a ganawarsa da AIT.
Yace sun san yanda ake yi, idan za’a yi taro ana bi kauyuka akwai wadanda ake baiwa kudi su rika tara maka mutane.
Yace a yanzu Abba ya shiga siyasar kasa inda yake damawa da sauran takwarorinsa.