Monday, April 6
Shadow

Na baku kwana 3, ko dai ku sakeni, ko kuma zaku nenemi ku rasa>>Faston nan na asar Ghana da yace za’a yi tashin Qiyama ranar Kirsimeti amma ba’a yi ba

Fasto Ebo Noah wanda ya ce wai an masa wahayi za’a yi tashin Qiyama ranar Kirsimeti, 25 ga watan Disamba amma ba’ayi ba, ya gargadi hukumomin kasar Ghana da suka kamashi.

Faston dai an kamashine saboda wannan abu da yayi ya dauki hankulan Duniya.

Saidai ya gargadi hukumomin kasar Ghana da cewa ya basu kwanaki 3 ko dai su sakeshi ko ya bace daga gidan yarin da ake tsare dashi.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya, NRC, ta dakatar da jigilar fasinja daga Kaduna zuwa Abuja

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *