
Wata mata me suna Akinyi Hellen na neman shawarar yanda zata yi da kanwarta uwa daya uba daya data kwanta da mijinta.
Tace iyayensu tun suna yara suka rabu dan haka ta dauki kannenta dan ta rikesu.
Tace ita ta saka kanwartata a makaranta har ta gama amma daga baya sai ta fara kwanciya da mijinta, tace ta tsani aure saboda tasan maza shedanune.


Tace kanwartata kuma sai tambayar mijinta kudi tace akai-akai.
Tace bata da wani wanda zata yi shawara dashi shiyasa ta wallafa a shafinta na Facebook take neman shawara.