
Dan gidan Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, watau Ibrahim El-Rufai ya bayyana cewa shi a wajansa, Musulmai da Kiristoci shedan suke bautawa.
Ya bayyana hakane a cikin Bidiyon sa da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda ya bayyana cewa shi bai yadda da Allah ba.
Ya kuma zargi mutanen Arewa da aurar da mata da wuri inda yace abin na ci masa tuwo a kwarya.