Thursday, February 5
Shadow

Rahotanni sun ce, Donald Trump ya fasa kawowa Najeriya Khari, Takunkumi zai kakaba mata

Wani dan majalisar kasar Amurka, Bill Huizenga ya bayyana cewa, Shugaban kasarsu, Donald Trump da wuya ya kawowa Najeriya hari.

Yace maganar da Trump yayi, ya yi tane cikin bacin rai da damuwar asarar rayukan da ake yi a Najeriya.

Yace amma Trump takunkumi ne zai kakabawa kasar da masu mulkarta wanda hakan zai fi kawo hari amfani.

Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Arise TV.

Yace Trump ba mutum ne me son tashin hankali ba saboda a baya ya baiwa sulhu da zaman lafiya muhimmanci fiye da tashin hankali dan haka ba zai kawo Hari Najeriya ba.

Karanta Wannan  Shugaba Tinubu yayi ikirarin cewa a lokacin da ya hau mulki Ana sayen dalar Amurka akan Naira 1,900 Saidai dai da yawa sun musanta wannan ikirarin na shugaban kasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *