Friday, December 5
Shadow

Sanata Natasha Akpoti zata gurfana a gaban kotu bisa karar da Gwamnatin Tarayya ta kaita na bata suna

A ranar Talata me zuwa ne ake sa ran Sanata Natasha Akpoti zata gurfana a gaban kotu.

Rahotanni sun bayyana cewa, Lauyan Sanata Natasha, West Idahosa (SAN) ne ya bayar da tabbacin.

Yace a matsayin sanata Natasha na ‘yar kasa ta gari me bin doka, zata bayyana a gaban kotun kamar yanda aka bukata.

Gwamnatin Tarayya ta shigar da karar Sanata Natasha Akpoti ne ta hannun wailinta, Mohammed Abubakar inda take zargin Natasha da bata suna.

Gwamnatin ta yi zargin Sanata Natasha Akpoti tace wai kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio da tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello sun yi yunkurin kasheta.

Sannan tace wai Sanata Godswill Akpabio yana safarar sassan jikin dan adam kamar yanda ta gayawa wata mata.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Ganin ana tallar maganin gargajiya da Motar Prado a Kano ya jawo cece-kuce

Daga cikin shaidun da gwamnatin tarayya zata gabatar a wannan karar, Akwai Sanata Godswill Akpabio da Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello da wasu mutane 4.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *