Friday, December 5
Shadow

Sanatan Amurka ya gabatar da kudirin dokar Hukunta wasu ‘yan Najeriya da jihohin Arewa 12 dake amfani da dokar shari’ar Musulunci

Sanatan Amurka, Ted Cruz wanda shine ya kai kudirin dokar da ta saka Najeriya cikin jerin kasashen da Amurkar ke sakawa ido bisa zargin anawa Kiristoci khisan Kyiyashi a yanzu kuma ya sake kai wani Kudirin dokar majalisar kasar.

Ted Cruz ya godewa shugaban kasa, Donald Trump kan matakin da ya dauka akan Najeriya inda yace a baya lokacin mulkin Trump na farko, ya saka Najeriya cikin kasashen da Amurka zata rika sakawa ido amma tsohon shugaban kasar, Biden ya cireta.

Saidai yace ya ji dadi da a yanzu Trump ya dawo da Najeriya cikin kasashen da Amurka zata rika sakawa ido.

Yace a yanzu ya sake gabatar da wata sabuwar kudirin doka da zata hukunta wasu ‘yan Najeriya da ake zargi da hannu wajan Muzgunawa Kiristoci sannan ya ce zakuma a dauki hukunci kan jihohi 12 na Arewa dake amfani da shari’ar Musulunci.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Wadannan Duka Infoma ne da aka kama a jihar Katsina

Hakanan yace zasu tabbatar an daina hukunta masu yin batanci ga addinin Musulunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *