Tuesday, February 24
Shadow

Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa sanatoci sun ce ya rokeshi ya sake duba janye musu jami’an tsaron da yayi.

Sanata Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu hakanne a yayin da shugaban ya je gabatar da kasafin kudin shekarar 2026a zauren majalisar.

A baya dai shugaba Tinubu ya bayar da umarnin janyewa duk wani babba a kasarnan jami’an tsaron ‘yansanda.

Karanta Wannan  A jihar Borno ma an gurfanar da kananan yara a gaban kotu bisa zargin shiga Zanga-zanga da batawa gwamna Zulum Suna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *