Friday, December 19
Shadow

Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa sanatoci sun ce ya rokeshi ya sake duba janye musu jami’an tsaron da yayi.

Sanata Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu hakanne a yayin da shugaban ya je gabatar da kasafin kudin shekarar 2026a zauren majalisar.

A baya dai shugaba Tinubu ya bayar da umarnin janyewa duk wani babba a kasarnan jami’an tsaron ‘yansanda.

Karanta Wannan  An yiwa Alkalan Najeriya 10 ritayar dole bayan samunsu da rage shekaru dan ci gaba da aiki

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *