Friday, January 16
Shadow

Shugaba Tinubu ya bar Katsina bayan ziyarar Kwanaki biyu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bar Katsina bayan kammala ziyarar kwanki biyu da ya je jihar.

D misalin karfe 3 na yammacin ranar Asabar ne jirgin shugaban kasar ya bar filin jirgin sama na Umar Musa ‘Yaradua dake jihar.

Shugaba Tinubu a yayjn ziyararsa a jihar Katsina ya ziyarci sojoji inda ya karfafa musu gwiwa sannan ya kaddamar da wasu ayyuka biyu na titi da wata cibiyar ayyukan noma da gwamnatin jihar ta gina.

A yau Asabar kuma shugaba Tinubu ya halarci daurin auren diyar gwamnan jihar Dikko Radda kamin barin Katsina.

Karanta Wannan  Masana Ilimin Taurari sunce wani katon dutse zaizo kusa da Duniyarmu, kuma za'a iya ganinsa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *