Thursday, January 15
Shadow

Shugaba Tinubu ya nemi Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya samo masa fili ya gina gidan da zai yi ritaya a jihe Anambra

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nemi gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya nemo masa filin da zai gina gidan da zai yi ritaya a jihar Anambra.

Shugaban ya bayyana hakane a yayin ziyarar sa ta farko a matsayin shugaban kasa a jihar ta Anambra inda ya kaddamar da ayyukan da gwamnatin jihar ta yi daban-daban.

Ya jinjinawa Gwamnan kan kokarin gyaran jihar da yake yi inda yace masa shima ya zama dan jihar Anambra a sama masa fili ya gina gidan da zai yi ritaya.

Shugaban dai ya fadi hakanne cikin raha.

Karanta Wannan  Lauyoyin Nnamdi Kanu sun bayyana cewa, basu yadda da Sakamakon gwajin Lafiyar da aka masa ba inda suka ce ko jininsa ba'a dauka ba ta yaya za'a ce yana da lafiyar da zai iya ci gaba da tsayawa a gaban kotu?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *