Friday, December 5
Shadow

Shugaba Tinubu ya nemi Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya samo masa fili ya gina gidan da zai yi ritaya a jihe Anambra

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nemi gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya nemo masa filin da zai gina gidan da zai yi ritaya a jihar Anambra.

Shugaban ya bayyana hakane a yayin ziyarar sa ta farko a matsayin shugaban kasa a jihar ta Anambra inda ya kaddamar da ayyukan da gwamnatin jihar ta yi daban-daban.

Ya jinjinawa Gwamnan kan kokarin gyaran jihar da yake yi inda yace masa shima ya zama dan jihar Anambra a sama masa fili ya gina gidan da zai yi ritaya.

Shugaban dai ya fadi hakanne cikin raha.

Karanta Wannan  Gwamnan Katsina ya ba da hutun aiki saboda ziyarar Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *