Friday, December 5
Shadow

Shugaba Tinubu ya suke Gawuna daga shugaban Kwamitin gudanarwa na jami’ar Bayero dake Kano

Shuagaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nada AVM Sadiq Ismail Kaita a matsayin sabon shugaban kwamitin gudanarwa na jami’ar Bayero dake Kano.

Kaita ya maye Dr. Nasiru Yusuf Gawunane a wannan mukami.

Gawuna kuma shine shugaban hukumar kula da gidaje ta kasa.

A sanarwar da kakakin shugaban kasa, Bayo Onanuga ya fitar Yace an cire gawuna daga shugabancin kwamitin gudanarwa na BUK ne dan ya mayar da hankali kan shugabancin hukumar kula da gidaje ta kasa

Gawuna dai na hannun damar tsohon shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne.

Karanta Wannan  Babu irin muguntar da Buhari bai shiryawa Tinubu ba dan ya fadi zaben 2023 amma da yake Allah na sonshi, ya tsallake>>Inji Ministan Abuja Wike

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *