Friday, December 5
Shadow

Shugaba Tinubu zai shiryawa ‘yan kwallon kwando mata da suka ciyo kofin kwallon Kwando na mata na Afrika liyafa ta musamman, da yawa sun fara cewa akwai yiyuwar suma shugaban zai musu kyautar daloli

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai gana da ‘yan kwallon kwado mata na Najeriya da ake kira da D’Tigress bayan da suka yi nasarar lashe kofin gasar kwallon kwando ta mata na Nahiyar Afrika.

Kamar dai yanda yawa ‘yan kwallon kafa mata, Super Falcons, shugaban ya sha alwashin tarbar ‘yan kwallon kwando mata, D’Tigress da kofin da suka ciwo.

A jiya, Lahadi ne dai D’Tigress suka lashe kofin bayan doke kasar Mali da ci 78-64 a wasan da suka buga a Abidjan, Côte d’Ivoire.

A sanarwar da me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya fitar a madadin shugaban kasar, yace shugaba Tinubu ya yabawa ‘yan kwallon mata.

Karanta Wannan  INNA LILLAHI WA'INNA ILAHI RAJI'UN: Ta Rasu A Yayin Haihuwa Sakamakon Ťìýàťà Da Aka Yi Mata, Bayan Mahaifiyarta Ta Samu Labarin, Isowarta Asibitin Ke Da Wuya Ita Ma Ta Yanke Jiki Ta Fadi Ta Ŕàśù Bayan Ta Ga Ģàwaŕ 'Yarta Ta

Shugaban, ya kuma jinjinawa me horas da ‘yan kwallon mata watau, Coach Rena Wakama.

Sannan yace kamar yanda ya karbi ‘yan mata masu kwallon kafa, Super Falcons, yana shirin tarbarsu suma a Abuja.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *