Thursday, December 25
Shadow

Shugaban Amurka Trump yace zai yi Amfani da kudaden Harajin da ya samu daga kasashen Duniya wajan rabawa ‘yan kasar Dala $2000 kowannensu

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, zai Rabawa mutanen kasarsa dala $2000 kowanne daga kudin Harajin da ya tara daga hannun kasashen Duniya.

Ya bayyana hakane a shafinsa na Truth social inda yace kasarsa ce kasa da aka fi girmamawa a tsakanin kasashen Duniya

Sannan ya yi alkawarin yin amfani da kudin Harajin wajan biyan bashin da ake bin kasar Amurka.

Saidai da yawa ‘yan kasar ta Amurka na shakka akan wannan ikirari nasa.

Karanta Wannan  Kamfanin Multichoice dake da tauraron dan adam na DSTV ya rage farashi daga dubu 20 zuwa dubu 10 bayan da ya tafka asarar kudade saboda mutane sun daina kallo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *