Friday, December 5
Shadow

Tabbas Ministan Kudi bashi da lafiya, kuma ta dan yi tsanani, amma ba shanyewar rabin jiki bace>>Fadar Shugaban kasa

Fadar shugaban kasa, ta tabbatar da cewa, ministan Kudi, Wale Edun Bashi da lafiya

Wata majiya daga fadar ta tabbatar wa da gidan jaridar Punchng hakan inda tace rashin lafiyar ta matsa masa.

Saidai tace ba Shanyewar rabin jiki bane sannan ba’a fitar dashi zuwa kasar waje ba, sannan shugaban kasa Bola Tinubu bai fara neman wanda zai maye gurbinsa ba.

Rahotanni sun ce Likitocin Najeriya ne ke kula da Ministan amma idan lamarin yayi kamari za’a iya fita dashi kasar waje.

Karanta Wannan  HOTUNA: An gudanar da shagalin ƙarshe na Auren Rarara da Aisha Humaira a daren jiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *