Saturday, March 15
Shadow

Tinubu ya amince da kasafin kammala titin Abuja-Kano cikin wata 12

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ba da umarnin kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano cikin wata 12.

Mai magana da yawun fadar shugaban Najeriya, Sunday Dare, ya ce a yau Litinin shugaban ya amince bayar da umarnin.

“Shugaba Tinubu ya amince da kasafin kammala wuraren da ba a gama ba a kan titin Abuja-Kaduna, da na Kaduna-Zaria cikin wata 12,” kamar yadda ya wallafa a shafinsa na dandalin X.

Ya ƙara da cewa “wannan titi ne mai muhimmanci ne a kodayaushe”.

A watan Janairu gwamnatin Bola Tinubu ta sanar da bai wa wani sabon kamfani ƙarashen aikin titin bayan ta ƙwace kwangilarsa daga hannun Julius Berger.

Karanta Wannan  DA DUMIDUMINSA: Jami'an Tsaro Sun Kara Samun Nasarar Hàĺĺàķà Wani Ƙasurgumin Ďan Bìñďìģa Mai Suna Ɓaleri Tare Ďa Yaransa Su 30 A Jihar Zamfara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *