Friday, December 5
Shadow

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTA

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTA

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi babban sauy-sauye na shugabanci a gidan talabijin na ƙasa, NTA, inda ya naɗa Rotimi Richard Pedro, a matsayin sabon Darakta-Janar na gidan talabijin din na gwamnati.

“Sauran manyan nade-naden sun haɗa da Karimah Bello daga Jihar Katsina a matsayin Daraktar Tallace-Tallace, Stella Din daga Jihar Filato a matsayin Daraktar Labarai, da kuma Sophia Issa Mohammed daga Jihar Adamawa a matsayin Babbar Darakta ta Kamfanin NTA Enterprises Limited.

“Pedro, ɗan asalin Legas, fitaccen mai kasuwanci a fannin kafafen watsa labarai da kuma mai ba da shawara, wanda ke da kusan shekaru talatin na kwarewar jagoranci a harkar watsa shirye-shirye, wasanni, da kuma tallace-tallace a faɗin Afirka, Birtaniya da Gabas ta Tsakiya,” in ji sanarwar.

Karanta Wannan  Mutane sama da dari biyu sun karbi Musulunci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *