Friday, December 26
Shadow

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTA

Tinubu ya naɗa sabon shugaban gidan talabijin na ƙasa, NTA

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi babban sauy-sauye na shugabanci a gidan talabijin na ƙasa, NTA, inda ya naɗa Rotimi Richard Pedro, a matsayin sabon Darakta-Janar na gidan talabijin din na gwamnati.

“Sauran manyan nade-naden sun haɗa da Karimah Bello daga Jihar Katsina a matsayin Daraktar Tallace-Tallace, Stella Din daga Jihar Filato a matsayin Daraktar Labarai, da kuma Sophia Issa Mohammed daga Jihar Adamawa a matsayin Babbar Darakta ta Kamfanin NTA Enterprises Limited.

“Pedro, ɗan asalin Legas, fitaccen mai kasuwanci a fannin kafafen watsa labarai da kuma mai ba da shawara, wanda ke da kusan shekaru talatin na kwarewar jagoranci a harkar watsa shirye-shirye, wasanni, da kuma tallace-tallace a faɗin Afirka, Birtaniya da Gabas ta Tsakiya,” in ji sanarwar.

Karanta Wannan  Na kusa da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu na karbar kudi(Cin Hanci) kamin su bayar da dama a ganshi>>Inji Sanata Ali Ndume

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *