Tuesday, August 11
Shadow

Da Duminsa: Majalisar Jihar Rivers ta fara shirin tsige gwamna Fubara

Rahotanni daga jihar Rivers sun bayyana cewa, Majalisar Jihar ta fara shirin tsige gwamnan jihar, Simi Fubara.

An ga kakakin majalisar a wani Bidiyo daya watsu sosai a kafafen sada zumunta yana cewa ‘yan majalisar 26 sun sakawa takardar neman tsige Fubara hannu.

Majalisar tace tana zargin Gwamna Fubara da karya dokar kundin tsarin Mulki.

Kuma sun ce zasu aika masa da takarda kan hakan.

Hakanan majalisar ta kuma ce ta fara shirin tsige mataimakin Gwamnan na jihar Rivers, Ngozi Nma Odu.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Yanda mawakin Najeriya Asake ya raba tallafin kayan abinci a Saudiyya ga mabukata

Majalisar ta kuma ce ta dakatar da shirin Gwamna Fubara na kai mata kasafin kudin shekarar 2026.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *