
Shugaba Donald Trump, na Amurka, ya yi barazanar zafafa yaƙin kasuwanci da ke tsakaninsu da China, ta hanyar kakaba karin harajin kashi 50 cikin 100 na kayayyakinsu, muddin Beijing ba ta jingine shirinta na mayar da martani ba.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump, ya ce zai kawo karshen duk wata yarjejeniya da ke tsakaninsu, muddin China ba ta yi biyayya ba.
Wannan harajin da Trump ke shirin sanya wa China zai haura kashi 100 cikin 100.
A mako mai zuwa ne haraje-harajen da China ta sanya ita ma kan kayayyakin Amurka za su soma aiki.