Monday, March 16
Shadow

Tsaffin sojoji da suka yi ritaya sun yi zanga-zangar rashin biyansu albashi

Tsaffin sojoji da suka yi ritaya ranar Talata sun kai kujeru da rumfa a kofar fishin ma’ikatar kudi dake Abuja inda suka yi zaman dirshan suka bukaci a biyasu hakkokinsu.

Dama dai a watan Disamba daya gabata, sojojin sun yi irin wannan zanga-zanga ta neman hakkinsu.

Watanni da yawa sun shude inda ake gayawa tsaffin sojojin cewa, babu kudin da za’a biyasu hakkokin nasu.

Bayan zanga-zangar da suka yi a watan Disamba, an biyasu kaso 50 cikin 100 na hakkokin nasu inda aka musu alkawarin biyan suran amma sunce har yanzu shiru.

Karanta Wannan  An yi min wahayin cewa, Tinubu ko shine da kansa zai zama shugaban INEC ba zai ci zaben 2027 ba muddin ya dage sai ya karbi Haraji a hannun 'yan Najeriya>>Inji Fasto Ayodele

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *