
Tsohuwar minister Jin kai, Betta Edu wadda aka sauke saboda zargin karkatar da kudaden talakawa ta bayyana a wajan bikin cika shekaru 50 da kafuwar jami’ar Calabar dake jihar Cross-River.
Wani abin mamaki shine har kyautar karramawa aka baiwa ministar.
Da yawa sun yi mamakin ganin Ministar a bainar jama’a tana ta sha’aninta.
Kyautar da aka bata itace ta tallafawa al’umma da ta yi.
Daga cikin zarge-zargen kudaden da akawa ministar a baya sun hada da na Naira Miliyan N585 da kuma na Dala $640,000.
A baya dai tsohuwar ministar ta kuma shiryawa Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero shan ruwa a gidanta.