Wednesday, April 9
Shadow

Tsohuwar Ministar Jin Kai, Betta Edu da aka sauke saboda zargin karkatar da kudin Talakawa ta samu kyautar girmamawa a jami’ar Calabar

Tsohuwar minister Jin kai, Betta Edu wadda aka sauke saboda zargin karkatar da kudaden talakawa ta bayyana a wajan bikin cika shekaru 50 da kafuwar jami’ar Calabar dake jihar Cross-River.

Wani abin mamaki shine har kyautar karramawa aka baiwa ministar.

Da yawa sun yi mamakin ganin Ministar a bainar jama’a tana ta sha’aninta.

Kyautar da aka bata itace ta tallafawa al’umma da ta yi.

Daga cikin zarge-zargen kudaden da akawa ministar a baya sun hada da na Naira Miliyan N585 da kuma na Dala $640,000.

A baya dai tsohuwar ministar ta kuma shiryawa Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero shan ruwa a gidanta.

Karanta Wannan  Hukumomin sojin Amurka sun sace kudin da aka ware dan ciyar da sojojin kasar Abinci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *