
Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Afirka ta Yamma, WAEC ta fitar da sakamakon jarrabawar 2025 a Najeriya.
Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce ta saki sakamakon ne a yau Litinin 4 ga watan Agustan 2025.
Hukumar ta kuma buƙaci ɗaliban da suka rubuta jarrabawar da su shiga shafinta na http://waecdirect.org. domin duba sakamakon jarrabawar tasu.