Friday, December 5
Shadow

Wasu ‘yan ADC sun maka su Atiku a kotu suna kalubalantar shugabancin jam’iyyar da aka baiwa David Mark

Wasu ‘yan jam’iyyar ADC sun maka sabbin Shuwagabannin jam’iyyar da aka nada na kwanannan a kotu inda suke neman kotun data bayyana ko shugabancin nasu ya halasta a doka?

Wadanda suka kai karan su 4 ne da suka hada da Adeyemi Emmanuel, Ayodeji Victor Tolu, da Haruna Ismaila.

Sun nemi kotun ta kuma hana hukumar zabe me zaman kanta INEC ta amince da sabbin shuwagabannin na riko.

David Mark ne aka baiwa shugaban jam’iyyar na riko sai kuma Rauf Aregbesola aka bashi sakataren jam’iyyar na riko.

Karanta Wannan  Ka shiga taitayinka, naga take-takenka baka a da'a>>Shugaba Tinubu ya gargadi Sanata Ali Ndume bayan da yace 'yan Najeriya na cikin wahala

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *