Saturday, May 10
Shadow

Wata Sabuwa: A yayin da suke shirin kulla alaka me karfi dan kwace mulki a 2027, an gano cewa Gwamnonin PDP sun daina daukar wayoyin Atiku da El-Rufai idan sun kirasu

Rahotanni sun bayyana cewa a yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke shirin kulla alaka me karfi dan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027, Gwamnonin PDP sun daina daga wayarsu idan sun kirasu.

Wani Jigo a jam’iyyar APC, Ayekooto Akindele ne ya bayyana hakan.

Yace Gwamnonin PDP irinsu Ademola Adeleke basa daukar wayar Atiku da El-Rufai da rana a yanzu.

Yana martanine kan rahoton dake cewa, Gwamnonin PDP din sun hada kai da Tinubu dan bashi goyon baya ya zarce a shekarar 2027.

Ya kara da cewa, Babu yadda Atiku da El-Rufai zasu iya hana Tinubu zama shugaban kasa a shekarar 2027.

Karanta Wannan  Ya kamata a jinjinawa Atiku Abubakar kan kokarin gyaran tattalin arzikin da yayi>>Inji El-Rufai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *