Wednesday, May 14
Shadow

Wata Sabuwa: An gano cewa, Kwankwaso da Peter Obi Tinubu sukawa aiki a zaben 2023 kuma akwai yiyuwar a 2027 ma zasu sake masa

Dan fafutuka kuma Lauya, Deji Adeyanju ya yi zargin cewa, Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da dan takarar shugaban kasa na Labour party, Peter Obi, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sukawa aiki a shekarar 2023.

Ya bayyana cewa kuma akwai yiyuwar a shekarar 2023 ma zasu sake yi masa.

Deji ya bayyana hakane a shafinsa na X inda yake sharhi game da hadakar ‘yan Adawa da ake shirin kullawa.

Yace idan ana son wannan hadaka ta yi aiki, sai Atiku da Peter Obi sun koma gefe sun bar wanda bai goyon bayan kowa ya jagoranci wannan tafiya.

Deji yace amma da wuya Peter Obi ya yadda a yi wata hadaka dashi

Karanta Wannan  Hotuna YANZU-YANZU: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Taho Da Yaran Jihar Kano Zuwa Gida Yanzu Haka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *