Wednesday, April 23
Shadow

Ya kamata a jinjinawa Atiku Abubakar kan kokarin gyaran tattalin arzikin da yayi>>Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ya kamata a jinjinawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar kan kokarin gyaran tattalin arzikin da yayi a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo.

Ya bayyana hakane a wajan gaisuwar marigayi, Edwin Clark a jihar Delta.

El-Rufai yace yawanci mutane sun fi tunawa da abin ashsha da mutum ya aikata fiye da abin alkairi.

El-Rufai yace hadda shi sun yi aiki a karkashin Atiku suka gyara tattalin arzikin kasarnan a lokacin amma ba’a magana akan lamarin ko dan basu yi rubutu akan lamarin bane?

Karanta Wannan  Ana zargin DPO da yin lalata da karamar yarinya me shekaru 15 da aka tsare a fishin 'yansanda a Katsina

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *