Saturday, May 24
Shadow

Ya kamata mutane su shiga taitayinsu su daina yada karya da bata sunan dan shugaban kasa, Seyi Tinubu>>Kungiyar Kiristoci ta CAN ta yi gargadi

Kungiyar Kiristoci ta CAN reshen Jihohin Arewa 19 da Abuja ta bayyana rashin jin dadinta kan yanda ake samun wasu suna batawa dan shugaban kasa, Seyi Tinubu suna da yada karya akansa.

Shugaban kungiyar, John Joseph Hayab ne ya bayyana hakan inda yace mutane su sani akwai rayuwa bayan mahaifinsa, Tinubu ya sauka daga shugaban kasa.

Ya kara da cewa, yada karya ya sabawa Al’ada da Addinin da muke bi.

Yace dan haka kamata yayi kafafen watsa labarai su rika tantance labari kamin su yadashi.

Karanta Wannan  Dan Gwamnan Jihar Neja, Marwan Bago Ya Zama Babban Matukin Jirgin Sama Na Kamfanin Jirage Na 'Overland Airways', Inda Har Ya Yi Sawu Daya Zuwa Abuja

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *