Thursday, April 10
Shadow

‘Yansanda sun Tarwatsa masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da ‘yan Jarida suka banka musu barkonon tsohuwa a jihar Rivers da Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yansanda a Jihar Rivers sun tarwatsa masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da suka fito a yau, Litinin.

Rahoton yace da misalin karfe 9 na safe ne matasan masu zanga-zangar suka fito inda suka ci karo da dandazon ‘yansanda a filin Isaac Boro Park dake birnin na Fatakwal.

‘Yansandan aun gayawa matasan cewa ba zasu barsu su yi zanga-zangar ba amma matasan sun ce sai sun yi.

‘Yansandan sun harbawa matasan barkonon tsohuwa sannan suka bisu da duka ciki hadda ‘yan jarida da suka je daukar lamarin.

Hakanan a babban birnin tarayya, Abuja ma, ‘yansandan sun bankawa matasa masu zanga-zangar barkonon tsohuwa da suka fito yin zanga-zangar a maitama.

Karanta Wannan  An shirya gagarumar zanga-zanga ranar 4 ga watan Fabrairu saboda karin kudin kiran waya da kaso 50

Wannan rana ta Zanga-zangar dai ta zo daidai da ranar ‘yansanda ta Najeriya.

Dan haka ne ma ‘yansandan suka nemi a dakatar da yin zanga-zangar amma wanda suka shiryata suka kiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *