Monday, March 16
Shadow

‘Yansandan Kano sun kama waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta ce ta kama wasu mutane da take zargi sun shiga jihar ne da nufin yin yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an kama mutanen a garin Kwanar Dangora, kuma yanzu suna hannun ‘yansanda, bayan da ya ya ce sun shiga jihar da nufin yin garkuwa da mutane.

Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce ”wannan kasuwancin fa na satar mutane ba zai yi tasiri a Jihar Kano ba Insha Allah”.

Ya kuma gode wa al’ummar jihar bia addu’o’in da ya ce suna yi a koyause.

Karanta Wannan  Furuciñ Da Na Yì Na Cewa Koda Añnàbì SAW Źaì Hana Maùludì Ni Sai Na Yi, Tabbas Ña Yi Kusķùrè Kuma Ina Rokon Alĺah Ya Yafe Mìn, Cewar Mawakin Yabo, Hafiz Abdallah

Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ba ta cikin jihohin yankin da ke fama da masu garkuwa da mutane, kodayake ana ɗan samu jifa-jifa, amma ba kamar sauran wasu jhohin yankin, da matsalar ta yi ƙamari ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *