Tuesday, February 3
Shadow

Yanzu-Yanzu: Bayan aiko da wakilanta suka ganewa idanunsu abinda ke faruwa a Najeriya, kasar Amurka tace lallai gaba dayan ‘yan Najeriya ne ya kamata a samarwa da tsaro

Dan majalisar kasar Amurka, Riley Moore wanda Shugaban kasar, Donald Trump ya wakilta ya zo Najeriya yaga yanda ake Mhuzghunawa Kiristoci kamar yanda suke zargi.

Bayan ziyarar tasa yace a yanzu ‘yan Najeriya gaba daya ne ya kamata a samarwa da tsaro.

Saidai yace duk da haka sun fi damuwa da samarwa Kiristoci tsaro.

Yace ya ji dadin yanda Najeriya ta amince zata yi aiki da kasar Amurka dan samarwa kasar tsaro amma ba a baki kawai abin ya kamata ya kasance ba.

Kamata yayi a tabbatar da abubuwan da aka tattauna a aikace.

Karanta Wannan  Wallahi Daga Yau Na Koma Dan Izala Ganin Yadda Wasu 'Yàñ Daŕìķà Kè Mùŕña Da Rasuwàr Śhèik Iďŕis Duťsèn Tanshi Saboda Bambancin Akìda Duk Da Cewa Malami Ne Na Mùsùlùncì, Inji Abubakar Aliyu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *