Wednesday, February 25
Shadow

Zamu sayar da matatun man fetur na kasarnan>>Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta bayyana aniyar sayar da matatun man fetur mallakin Gwamnati, watau na Kaduna, Fatakwal, da Warri.

Gwamnatin tace zata yi hakanne dan inganta aikin matatun da kuma jawo masu zuba jari Najeriya.

Babban me baiwa shugaban kasar shawara akan makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana hakan a wajan wani taro a Kasar UAE.

Matatun man fetur din na Najeriya sun lakume makudan kudade wanda aka ware dan gyarasu amma har yanzu basu aiki yanda ya kamata.

Karanta Wannan  MASHA ALLAH: Kakakin 'Yan Sandan Jihar Kano, Abdullahi Kiyawa Ya Ce Sakon Neman Shamsiyya Da Aure Da Nake Yi Ya Riske Su, Amma Sai Sun Gudanar Da Kwakkwarar Bincike Gudun Kada A Hada Tawagar Da Za Ta Fi Karfinsu Nan Gaba, Inji Dogo Yaro Crypto Yola

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *