Friday, December 5
Shadow

Ƴan bindiga sun kashe sojoji shida a wani hari kan bututun mai a Nijar

Wasu ƴan bindiga sun kai wa wata tawagar sojoji da ke sintirin aikin sa ido kan bututun man fetur a garin Tibiri da ke yankin Dosso a kudu maso yammacin Nijar harin kwantan ɓauna inda suka kashe sojoji akalla shida.

Rahoton wanda aka wallafa a shafukan sada zumunta ya kara da cewa soja ɗaya ya ɓata sannan an lalata motoci biyu a harin.

Rahoton bai bayyana ko an samu asarar rai a ɓangaren ƴan bindigar ba, ko kuma bayyana alakarsu da wasu ƙungiyoyi.

Ƴan bindiga dai sun kasance suna gudanar da ayyukansu a wasu sassan Nijar da ke kan iyaka da arewa maso yammacin Najeriya.

Har yanzu dai rundunar sojin ƙasar ba ta fitar da wata sanarwa kan harin ba.

Karanta Wannan  Hoto: Sojojin Najeriya sun kai samame inda suka kashe 'yan ta'adda 6 a Kaduna

Tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Yulin 2023, al’amuran tsaron ƙasar Nijar ke ƙara taɓarɓarewa, inda a lokuta da dama kungiyoyin masu dauke da makamai da masu iƙirarin jihadi ke kai hari kan jami’an tsaro da fararen hula.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *