Friday, December 5
Shadow

Ƴànbìndìgà sun yi gàrkùwà da mata 25 a hanyar zuwa biki a Zamfara

Rahotanni daga jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa, ƴan bindiga sun yi garkuwa da aƙalla mata 25 a garin Kurmi na ƙaramar hukumar Maru

An ce dai an yi garkuwa da matan ne suna kan hanyar zuwa gidan bikin.

Haka ma wasu ƴan bindigar sun yi garkuwa da aƙalla mutum 19 yayin da suka raunata ƙarin wasu da dama, a garin Galadi da ke ƙaramar hukumar Tsafe, duk dai a jihar ta Zamfara.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo:Jama'ar Katsina ku yi Hakuri, kamin in hau mulki na yi Alkawarin duk wata zan rika bada bayanin yawan kudaden da muka samu da yawan wanda muka kashe, amma yanzu da na zama Gwamnan naga abin ba zai yiyu ba>>Inji Gwamnan Jihar Katsina Dikko Radda

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *