Tuesday, May 20
Shadow

Masu Gàrkùwà da mutane sun sace dalibai 2 a kofar makarantarsu

Rahotanni daga Makurdi Jihar Benue na cewa masu garkuwa da mutane sun sace dalibai biyu daga jami’ar Joseph Sarwuan Tarka University dake jihar.

An yi garkuwa da dalibanne a daren ranar Talata a gaban makarantarsu.

A hirar da aka yi da daya daga cikin daliban me suna Ashar Lubem ya bayyana cewa dalibai 4 ne aka yi garkuwa dasu kuma lamarin ya jefa daliban makarantar cikin rudani.

Kakakin ‘yansandan jihar, Sewuese Anene ta tabbatar da faruwar lamarin saidai tace dalibai 2 ne kadai aka yi garkuwa dasu kamar yanda suka samu bayanai.

tace kuma suna kan binciken lamarin.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo yanda mutane ke guduwa daga karamar hukumar Ryom ta jihar Filato dan fargabar kai hàri

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *