Tuesday, April 7
Shadow

Yanda Sanata Akpabio Ya taba rike hannuna a gaban mijina>>Sanata Natasha Akpoti

Sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi ta bayar da labarin yanda Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya taba rike hannunta a gaban mijinta.

Tace a lokacin sun je taya Akpabio murnar zagayowar ranar haihuwarsa ne inda mijinta ya rakata.

Tace Sanata Akpabio ya kama hannunta ya jata ya rika nuna mata gidansa yayin da mijinta ke binsu a baya.

Tace abin ya damu mijinta a lokacin wanda daga nan ya rika cewa ba zata rika yin tafiya ita kadai ba.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa: An gano Makudan kudaden da shugaba Tinubu ya ware Kusa Tiriliyan 2 na gyaran Titunan Najeriya, Fiyade da rabin kudin Legas da kudancin Najeriya za'awa aiki dasu inda Arewa ta samu kaso kadan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *