Monday, March 24
Shadow

GWAMNATIN JIHAR KEBBI TA AURARDA ‘YA’YA MATA 300 (DA MAZAJENSU) KARO NA 2 !

A jiya Alhamis ne (27/02/2025) Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin zababben Gwamnan Jihar (Comr. Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu) ta sake daurawa mata 300 aure da mazajensu , tareda duk abinda ya dace ayi musu na karramawa (auren gata kenan).

Wannan kudurin (na shirin auren gata) mai girma Gwamnan Jihar Kebbi ya sanya shi a ransa , cewa da ikon Allah zai yi iya na shi kokari don ganin gwamnatinsa ta ci gaba da bada irin wannan gudummuwa musamman ga marasa karfi , don taimakawa al’umma wajen rage yawan gwagware da kuma rage yaduwar alfasha a cikin al’umma.

Ko shakka babu wannan ba karamin alkhairi bane a cikin al’umma musamman idan sun gano hadarin da ke cikin yawaitar mabukata aure mata/maza kuma ba suda halin yin auren , a irin wannan lokacin komai na iya faruwa a kowane bangaren. !

Karanta Wannan  Yawanci masu sharhi akan dakatar da sanata Natasha Akpoti jahilaine, kamar wanda ba musulmi bane yace zai fassara Qur'ani>>Sanata Godswill Akpabio

Muna addu’a Ubangiji Allah ya sakawa mai girma Gwamnan Jihar Kebbi da mafificin alkhairi ya kara taimakonsa a cikin wannan Gwamnatin tasa , ya iya masa da iyawarsa , kar ya barshi da iyawarsa, ya Allah kar ka ba azzalumai nasara akansa.

Wa’yannan aurarraki da aka daura muna addu’a Ubangiji Allah ya sanya alkhairai masu yawa a cikinsa , kuma ya sa Gwamnatin Jihar Kebbi tayi alfahari da shi.

Sani Musa Saminaka,
Mataimaki na musamman ga mai girma Gwamnan Jihar Kebbi (ta hanyoyin sadarwa na zamani).

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *