Wednesday, May 21
Shadow

Najeriya ta zo ta shida a cikin kasashen da aka fi aikata ayyukan tà’àdàncì a Duniya na shekarar 2025

Najeriya ce ta zo matsayi na 6 a cikin kasashen da aka fi aikata ayyukan ta’addanci a Duniya a shekarar 2025.

A shekarun 2023 da 2024 Najeriya tana matsayi na 8 ne.

Kasar Burkina Faso ce ta zo a matsayi na farko sai kuma kasar Pakistan na biye mata baya inda kasar Syria ta zo ta 3.

Mali ce ta 4 sai kasar Nijar ta 5 sai Najeriya ta zo ta 6.

Hakanan rahoton yace an samu yawan mutanen da aka kashe ta sanadiyyar ta’addanci a Najeriya wanda yawansu ya kai mutane 565 jimulla.

Karanta Wannan  Gwamnatin tarayya ta samu Naira Biliyan 84 daga kudin harajin Naira 50 da take cirewa akan duk Dubu 10 da 'yan Najeriya suke fire daga Bankinsu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *